Malamai
Ya Kamata Masu Aure Su Dinga Fita Cin Shawarma Da Pizza Da Matansu ~ Dr Abdallah Gadon Kaya
Dr Abdallah Usman Umar, limamin masallacin Usman Bin Affan da ke Unguwar Gadon Kaya, ya ce ya kamata magidanta su dinga fita tare da matansu zuwa wurin cin abinci don hakan ya na kara dankon soyayya sannan kuma kyautatawa ce ta masoya.
Dakta Abdallah ya kara da cewa idan namiji yana yin hakan zai kara shakuwa tsakaninsa da matarsa.
Ya shaida hakan ne a wani shiri na Dala FM na Rayuwa Abar Koyi da ya gudanar a ranar Juma’a.
Kamar yadda yace:
“Magidanci zai samu shakuwa da kyautatawa tsakaninsa da matarsa idan har yana fita tare da ita zuwa wurin cin abinci tare da zagawa da ita cikin gari musamman wuraren da bata sani ba.”
Ya kara da cewa:
“Bai kamata mazajen aure su dinga yin saurin fushi tsakaninsu da matansu ba, ya kamata su dinga hakuri maimakon yin hakan.”
Dakta Abdallah ya kara da cewa idan namiji yana yin hakan zai kara shakuwa tsakaninsa da matarsa.
Ya shaida hakan ne a wani shiri na Dala FM na Rayuwa Abar Koyi da ya gudanar a ranar Juma’a.
Kamar yadda yace:
“Magidanci zai samu shakuwa da kyautatawa tsakaninsa da matarsa idan har yana fita tare da ita zuwa wurin cin abinci tare da zagawa da ita cikin gari musamman wuraren da bata sani ba.”
Ya kara da cewa:
“Bai kamata mazajen aure su dinga yin saurin fushi tsakaninsu da matansu ba, ya kamata su dinga hakuri maimakon yin hakan.”
Www.labarai.com.ng