#HamisuBreakerKannywood News
Kaunar Danake Yiwa Annabi Ce Tasa Nayi Wakar Yabonsa Inji Stephanie DadinKowa – Labarai.com.ng
Fitacciyar jarumar fina -finan Hausa a cikin shirin DadinKowa na gidan talabijin na Arewa24, Sarah Aloysius wadda wasu sukafi sani da Stephanie DadinKowa, ta ce matuƙar girmamawar da take yi wa Annabin Musulunci, Muhammad (S. A. W) ne ta sa aka ganta tana rera wakokin yabonsa cikin harshen Larabci a wani faifan bidiyo a shafinta na TikTok.
Jarumar wadda mabiyiya addinin kiristanci ce, wacce aka fi sani da Stephanie, ita ma ta bi sahun miliyoyin al’ummar musulmai a sassan duniya domin gudanar da bikin Maulidin Annabi duk da asalin addinin ta.
Www.labarai.com.ng