Uncategorized

Ƙungiyar Kiristoci ta ƙasa CAN, ta bayyana rashin amincewarta akan sauya ranakun aiki zuwa kwanaki huɗu a Jihar Kaduna.

 

Ƙungiyar Kiristici ta ƙasa CAN reshen Jihar Kaduna ta hau teburin naƙi dangane da kuɗirin Gwamna El-Rufai na mayarda ranakun aiki kwana huɗu, tare da zargin cewa akwai boyayyen shiri a lamarin.

A ranar Litinin ne Gwamnan ya bayyana ƙudirin Gwamnatinsa cewa an cire ranar Juma’a daga cikin ranakun aiki a faɗin Jihar, kuɗirin da zai fara wanzuwa a gobe 1 ga watan Disamba 2021.

Yayin sharhi dangane da lamarin, Shugaban ƙungiyar ta Kiristoci CAN mai suna John Joseph-Hayab yayi jaje tare da yin Allah-wadai bisa ga irin ƙudure-ƙuduren da Gwamnan yake bijirowa dasu a Jihar.

Mista Hayab, yayi kira ga ɗaukacin ma’aikata a faɗin Jihar akan kar su fara murna har sai sun tabbatar babu wata ɓoyayyen manufa a lamarin.

Www.labarai.com.ng

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button
Danna nan ga bidiyon
error: Content is protected !!